Bagdadi wanda asalin sunansa shi ne Ibrahim al-Samirrai ya bukaci mayakan Daesh wadanda suka ja daga da sojojin kasar Iraqi da masu tallafa masu kan cewa su daga da jihadi don nasara tana gabansu.
Duk da cewa har yanzun ba'a tantance ingancin sautinsa ba amma Bagdadi ya yi kira ga mayakansa da su kwararar da jinin wadanda ya kira kafirai a cikin kasar Iraqi su kuma maida dararensu rana.
A ranar 17 ga watan Octoban da ya gabata ne Rundunar sojojin kasar Iraqi tare da mayakan sa kai na Hashdushaabi da kuma na wasu kasashen waje suka fara farmakin kwatar tungar mayakan Daesh na karshe a kasar Iraqi, wato birnin Musil.
Yawan mutane a birnin dai sun kai miliyon 1.5 kuma tun shekara ta 2014 Daes take mamaye da birnin a matsayin cibiyar ta na abinda ta kira daular musulunci.288